Wasu 'Yan Kungiyar Boko Haram Sun Mika Kansu Ga Rundunar Sojoji A Borno
Wasu cikin 'yan Boko Haram da suka mika kansu da kansu
Rundunar ta ba mutane ukku cikin goman damar yiwa 'yan jarida bayani. Sun tabbatarwa 'yan jarida cewa lallai su 'yan Boko Haram ne da yanzu suka mika kai tare da yin nadama.
Mutanen sun bayyana cewa rayuwarsu ta jeji ba rayuwa ba ce. Sun ba gwamnati da 'yan Najeriya hakuri. Daya daga cikinsu baya Hausa yayi turanci ne. Yace sunansa Joseph David amma kungiyar ta sa masa suna Ibrahim Alechi. Ya yaba da yadda sojojin suka kula dashi lamarin da ya bashi mamaki domin bai yi tsammanin haka ba. Ya godewa Ubangiji da sojojin. Ya kira wadanda suke daji da su fito suma su mika kansu domin ba za'a kashesu ba.

No comments